Tuesday, 2 January 2018

KANASO A AMSA ADDU'ARKA ???

Tags

KANASO A AMSA ADDU'ARKA ???

Annabi (saw) yace:

Mutun uku idan sukayi addua ba'a dawo ita ana amsata alokacin sune:

1. Wanda aka zalunta yanemi agaji awajen Allah.

2.wanda yake yawan zikiri (ambaton Allah)

3. Shugaba adali mai adalci ga jamaarsa.

Tambihi:
Dayawa muna daukar cewa kalmar shugabanci ta rataye akan masu riqe da muqaman siyasa.

To a gaskiya abin ba haka yake ba.

A matsayinka na magidanci kaima shugabane, amatsayinki na matar gida kema shugaba ce.

Awani hadith manzon Allah (s.a.w) yana cewa:

كلكم راع وكلكم مسؤل أن رعيته

"DUKKANIN KU MASU KIWO NE KUMA DUKKANINKU SAI AN TAMBAYEKU AKAN ABIN DA AKA BAKU KIWO"

Allah ya gafarta mana zunubanmu baki daya.