WANENE ABDULLAHI BN MAS'UD [RA] ???
=====================
Abdullahi Bn Mas'ud Yana daya daga cikin wadanda suka fara musulunta tun kafin Annabi [S.A.W] yashiga gidan Arkam bn Abul Arkam.
Sababin musuluntar tasa kuwa shine a lokacin dayake kiwon dabbobi a Makka Annabi [SAW] yazo wucewa shida Abubakar [RA], sai ya tambaye shi yabasu nono.
Sai yace:
"Dukkan dabbobin basuda nono".
Sai Annabi [SAW] yasanya hannunsa ya ambaci sunan Allah take nonon ya bulbulo, dukkan su suka sha suka Qoshi.
Wannan abu da Abdullahi yagani sai mamaki ya
rufeshi, yace da Annabi [SAW].
"koya min abinda kafada haka ta kasance".
Sai Annabi [SAW] ya koyar dashi surori 70 daga bakinsa.
Yayi hijira sau 2, ya halarci yakin Badar da dukkan yaqoqi tareda Annabi [SAW].
Yana cikin manyan hadiman Annabi [SAW].
Shine gaba da kowa wajen iya karanta Al-qur'ani.
Shine Mutum na farko daya fara bayyanar da karatun alqur'ani a fili agaban mushrikan Makkah.
A zamanin Umar [RA] ya turashi kufa domin yadinga karantar dasu alqur'ani da hukuncin shari'ah.
Zan dakata anan.
Allah yakara masa yarda, sannan yaqara mana sonsu.
Thursday, 15 June 2017
WANENE ABDULLAHI BN MAS'UD [RA] ???
Tags
Artikel Terkait
This Is The Oldest Page
Post a Comment
Subscribe to:
Post Comments (Atom)